Thursday 10 August 2017

RYM 12

         Rayuwar      

              'Ya

           Mace           

Na Billy Ladan

*EXCLUSIVE* *WRITERS* *FORUM*

*12*

bintladan.blogspot.com

_Wannan shafin nakune,kungiyata abun alfaharina *EXCLUSIVE WRITERS FORUM* U guys r lyk family, I heart u ol_

Marin da Sabbura ta sauke wa MK shi ya jawo hankulan mutane, kan kace meh an taru a gefensu, nunosa tayi da yatsa tace "ga ka babban  mahaukaci, maras tarbiya wanda baisan mutuncin nagaba da shi ba, ai a haife wannan bawan Allah ya isa yayi jika da kai amma dan rashin 'da'a ka daga hannu ka sharara mai mari, uban meh kake takama da shi,kudi ko meh? Wlhy ka canza kidi dan rawarka ta sauya dan wannan ba dabi'a bace in kana yi a wani waje ana kyaleka toh irinmu baxa mu gani mu kyale ba kuma ka bi dunia a hankali dan gaba baka san da wa zaka hadu ba.

Mayar da hankalinta gun tsohon tayi da haryanxu yana rike da kumatunsa tace " Baba ina zaka yine? "Gomari zani ya bata amsa, tace " toh muje Baba in saka a mota, riko sandarsa tayi dan yi mai jagora, ya juyo gun MK da kunya ta gama lullubesa ganin yawan mutanen da ke wajen ciki harda boys nasa yace " 'dana duniyace, ta ishi kowa darasi in kayi mai kyau dan kanka in kuma kayi akasin haka duk wa kanka kuma ka guji bakin manya dan tamkar guba take a gareku yara, ya juyo gun Sabbura yace "ke kuma yata Allah ya miki albarka, Allah yasa ki gama da dunia lafia, Allah ya baki miji nagari da 'ya'ya ma su jin kanki, " amin" ta amsa mai tana mai jin dadin addu'arsa sannan ta wuce ta sashi a napep ta ciro naira hamsin da ta mallaka ta bawa mai napep in yayinda tsohon ke ta sa mata albarka.

Bata ko dubi inda MK yake ba tayi sauri ta shiga kwanar gidansu Atika, tana shiga soron gidan ta sunkuya tareda rike xuciyanta numfasinta sai fita yake da sauri sauri, mamakin kanta take da har ta iya marin MK tareda gaya mai maganganu son ranta abunda bata taba yi ba amma ko ba komai yau ta huce haushi tunda ta rama abunda yake mata.

MK kuwa mutuwar tsaye yayi a wajen, maganganunta bai bata mai rai kamar marin da ta mai ba, lalle kuwa yarinyar nan ta jawa kanta bala'i ya fada cikin ransa, juyawa yayi gun mutanen da suka tsaya suna kallonsa ya daka musu tsawa duk suka watse, abokansa ne suka karaso wajensa shima harara ya bisu da shi suna mai magana yayi banza da su ya shiga motarsa ya figeta cikin zafin nama, bai tsaya a ko ina ba sai gidan Nicky.

Falonta ya shiga ya zauna bai ma sanar da ita shigowansa ba, jinginar da kansa yayi a jikin kujerar yayinda ya daura kafa daya kan daya, daya kafar sai jijjigata yake, rufe idonsa yayi yayinda yake gano kwayar idonta lokacin da ta maresa ta kuma tsaya ta gaya mai magana son ranta, bude idonsa yayi naga har sun canza kala sunyi ja cikin bacin rai ya dunkule hannunsa ya kai wa center table da ke gabansa naushi wanda hakan yayi sanadiyar fashewarsa da yankewar hannunsa amma sam bai damu ba, jin karar ya sa Nicky fitowa cikin shirinta dan dama ta shirya, jiransa kawai take yazo su fita.

Ganin abunda ya faru ya sata karasowa da sauri ta rikosa tana "MK wts wrong? Jawota yayi ta fada jikinsa ya fara kissing nata dan shine kadai abunda yake ji zai kwantar mai da hankali ya dauke mai tunanin wancan aljanar. Da kyar Nicky ta kwaci kanta daga jikinsa ta riko hannunsa ta ce "MK u r bleeding ka tashi muje asibiti, tsaki yayi yayinda ya tashi ya wuce dakinta, binsa tayi itama ta bude drawernta ta ciro wani dankwalinta ta zo ta zauna gefensa ta dago hannun da ke ta zubar da jini ta daure mai ta gama ta juyo taga har yayi bacci tashi tayi ta cire kayanta ta sa na shan iska ta haye gado, ji tayi ya fara magana cikin bacci yana cewa " ku tabbatar kowaye ita kun kamota kun kawo mun ita a daren nan nake son ganinta in ba haka ba ranku zaiyi mugun baci, bugesa ta danyi sai gashi ya farka dan dama baiyi nisa ba, rai a bace tace "wa kake cewa za a kawo ma a bacci?, so duk abunda nake ma bai isheka ba kana neman wata MK toh wlhy baka isa ba, i gv u everything, jst bcs of u na daina kula kowa sai kai i was willing to gv everything up just to b with u but u nva sim to notice ba ka daukeni a matsayin komai ba sai wanda zaka huta da ita kawai n i wunt tk dt cos i want more n baka isa ka kula wata ba in as much as ina raye, tsaki yayi tareda tashi ya zauna yana mata kallon raini yace " i hv no idea maganar meh kike, in ma wani abun kika ji toh ki tattara ki zubar dan ni MK mata basu gabana dats y kika ga har yau bnyi aure ba kuma bnda ra'ayin yi kuma ds shld b d last tym da ina bacci zaki tasheni kuma ki sani ba ke kadai zan iya kai wa matsalata ta biya mun bukata ba so dnt lt ur hopes up in ma gani kike zan aureki o sumtn lyk dt gwara ki aje gefe in kuma dts wt u r after zn iya barinki in nemi wanda bazata na tayar mun da hankali ba, matsowa tayi da sauri ta riko hannunsa tace "am sorry dear bazan sake maganar ba dan Nicky na bala'in son MK kuma bata jin zata iya rabuwa da shi, kawar da kansa yayi ta kamo fuskansa ta juyo, ganin hannun mutum kwance a fuskansa ya sata shafa wajen cikin nuna kulawa tace " My luv wa ya mareka a nan? janye jikinsa yayi tareda sauka a kan gadon, gaban mirrornta ya nufa ya tsaya yana duba fuskarsa sai yanzu yaga hannun Sabbura kwance a fuskansa, hannunsa mai ciwon ya daga ya naushi jikin drawernta da shi, azabar da ya ziyarceshi shi ya sa shi yin baya tareda riko hannunsa, da sauri Nicky ta sauko ta karasa inda yake dunkule a kasa tana mai sannu, tashi yayi ya ja shirt nasa ya fice batareda ya ce da ita komai ba.

Da kyar ya iya driving kansa ya iso gida yana shiga gida bai yarda ya hadu da kowa ba ya shige dakinsa,toilet ya fada ya sake wa kansa shower, hannu ya sa ya shafi  inda Sabbura ta maresa sannan ya kai dubansa ga hannunsa da har yanzu yake fitar da jini kadan kadan yace "kamar yadda a dalilinki na samu wannan tabo toh wlhy kema sai na miki tabon da har ki mutu baza ki iya gogewa ba. Hannunsa na zafi haka ya daure ya wanke wajen ya fito ya shirya ya wuce aid box nasu yayi dressing sannan ya koma sama, yinin ranar a daki yayi dan baya so iyayensa su ga fuskansa.

Har bacci ya fara daukansa yaji bugun kofarsa ya taso ya bude, ganin boys nasa ya sa ya mayar da kofar zai rufe amma suka rike suna haba MK ka sauraremu mana, bude kofar yayi tareda yin gefe dan su shige suna gama shiga ya rufo kofarsa ya koma kan gadonsa, ganin hannun Sabbura kwance kan fuskarsa ya sa su fashewa da dariya wanda hakan ya dada kular da MK yayinda yake kara jin tsanar Sabbura a ransa dan ko ba komai ta gama zubar dashi a gaban boys nasa, juya musu baya yayi yace " in kun gama dariyarku zaku iya fita, shiru sukayi sannan babbansu yace "Wlhy MK Sabbura tayi da kai amma ba laifinta bane ba ta san ko kai waye bane shi yasa, juyowa yayi yana mai maimaita sunan " Sabbura" kai ya daga mai yace dts her name, dariyane ya kubce wa MK, ganin yana dariya suma suka biye mai, da kyar ya iya tsaida dariyarsa yace "wannan wani irin suna ne, sai kace yar tsintuwa, " inaga sunan larabcine" dayan ya bashi ansa, dariya MK ya cigaba dayi yace "duk da ba larabcin nake ji ba i doubt if sunan larabcine wannan ya karashe yana dariya, but anyways ko ma me take da suna zata gane kuranta zata san ta tabo MK zata kuma san ba a mun in bari, kuma bana barinta ta kwana sabida haka inaso in baku wani aiki, tashi yayi ya bude drowernsa ya ciro wani akwati ya zo ya aje a gabansu ya bude, ganin yawan kudin da yake ciki sai da duk suka razana, murmushin mugunta yayi sannan yace " ku dauka kuje zan turo muku da text in abunda nakeso kuyi da kuma inda zaku sameni bayan kun gama, hannu na rawa suka dauki akwatin tareda sara mai babbansu yace "muna jira oganmu, hannu kawai ya daga musu sukayi waje. Suna fita shima ya dauki key ya fice ya bar gidan.

Ayi hakuri da wannan

Billy Ladan ce

Share:

Monday 7 August 2017

RYM 7

🤦🏾‍♀         *Rayuwar*        🤦🏾‍♀

          🙆🏾       *'Ya*    🙆🏾

🙎🏽            *Mace*              🙎🏽

Na B.A. Ladan

♻ *EXCLUSIVE* *WRITERS* *FORUM*

*07*

Firgigit ya tashi, ba karamin bugawa zuciyarsa tayi ba ganin Rufaida tsaye a bakin kofarsa, juyawa yayi gun Nicky da tayi zuru zuru da ido ya mata wani banzan kallo sannan ya tashi dan sa kayansa ficewa Rufaida tayi idonta na zubar hawaye.

Da sauri ya gama sa kayansa ya bi bayanta, hr ya kusa kofa ya juyo yace "I always tell u to liv as early as possible amma baki ji so dnt b here wen i cm bk n kr ki sake zuwa sai na nemeki, yana ficewa itama ta tattara kayanta ta fice.

A hnkali ya turo kofarta ya shigo tareda sallama, can kan gado ya gnta rakube fuskarta na kallon gefe amma hakan bai hanashi gano hawayen da ke bin kuncinta ba, cikin sanyin jiki ya karaso ya zauna gefenta tareda kwantar da kansa a cinyarta shima ya fara kuka haka sukayi tayi hr kusan minti biyar ba wanda ya budi baki, can MK ya dago ya share hawayensa sannan ya kai hannunsa kan na yayartasa ya rike "am sorry sis, pls kar kice zaki tafi ki barni wlhy sharrin shaidan ne, i promise u wnt eva see dt again but pls dnt liv me ya fada yana hawaye, juyowa tayi ta kallesa da jajayen idanunta tace "MK tafiya dole inyi but abu daya zan gayama wannan sabon rayuwa da ka dauka ba rayuwa bace n if ka ce zaka cigaba a haka toh ka sani ka fada hanyar halaka, da kasan girman wannan zunubi da kake aikatawa da baka yi ko mafarkin aikatasa ba, ina mai baka shawara ka yarda wannan rayuwa tun wuri in kuma ka ki wlhy ba ni ba kai kuma in na sa kafa na fice a gidannan bazaka sake gani ba ko daddy sai dai muna gaisawa ta waya, indai rayuwar da ka zaba kenan toh ka sani bani ba kai mantawa zanyi inada wani kani tana gama fadin haka ta juya mai baya tayi kwanciyarta tace " ka fita bacci zanyi, cikin sanyin jiki ya fice ya bar dakin dan tunda suke bai taba ganin bacin ranta ba sai yau kuma sanin shi ya ja ba karamin damunsa yayi ba, yau ma tsautsayi ya sa ya kawo nicky gida if not can gidanta suke haduwa su gama abunda zasuyi ya dawo kuma ba wanda ya san wannan rayuwar da ya dau wa kansa. Dakinsa ya wuce ya dauki key ya fice.

Gefen gidansu Sabbura naga yayi parking ya fito ya nufi shagon da ke kallon gidansu, samarin da ke wajen suna hangoshi suka fara "MK!!!! har ya karaso basu bar ihun sunansa ba, daya daga cikinsu ne ya tashi ya ja mai kujera ya zauna tareda mika musu hannu suka gaisa, daya daga cikinsu yace " ya dai MK naganka wani sukuku haka hop lafia, ajiyar zuciya yayi sannan yace "my guy bari kawai ina cikin wata yar damuwa ne but komai wl b normal soon, miko masa taban da yake sha yayi tareda cewa "zuka daya ya isa ya tarwatsa duk wata damuwarka, dariya MK yayi tareda kawar da kansa yace " ai wannan sai ku, ka san bn wannan harkar taku,ni kunga tafiyata ma kr ku cutar da ni da hayakin sigarin naku, ya tashi yana mika musu hannu daidai lokacin Sabbura ta shigo shagon da sallamarta cikin shirinta na islamia, ko kallon gefensu batayi ba ta siya abunda zata siya ta zo zata fice ta kusa cin karo da MK da ke kokarin fita, ja da baya tayi dan ya wuce shikuwa hararanta yayi tareda jan wani tsaki sannan ya fice, tabe baki tayi dan ta ganesa kuma shima ya ganeta dukda nikabin da ke jikinta, a zuciyanta tana tunanin irin wannan halin na MK, yau dai yaci darajar shigar da ke jikinta if not da sai ta gaya mai magana dan ta tsani tsaki a rayuwarta, har ta fito bai bar wajen ba yana tsaye jikin motarsa yana waya yayinda hannunsa ke kan kofar motar, kallo daya ta mai ta kau da kai ta cigaba da tafiyarta yayinda shikuwa yabi bayanta da kallo yana mamakinta ace mutum kullum kana wani lullube kanka, sai da ya daina ganinta ya shige motarsa yana mamakin tsayawa da ya yi yana kallonta.

*WANENE MK*?

*Muhammad Kabir Mansur* shine asalin sunansa  'da na biyu ga Alhaji Mansur Bilyamin, kyakkyawa ne ajin farko yanada tsayi sosai ga kuma haske da Allah ya mishi wane balarabe, su biyu iyayensu suka haifa shida Yarsa Rufaida, bayan su iyayensu ba su sake haifuwa ba, aiki ya kai Abbansu Korea inda suma a can suka yi yawancin rayuwarsu dan MK ma a can aka haifesa.

MK na da shekara goma mahaifiyarsu ta bar gidan, haka kawai suka wayi gari suka ga bata nan, dalilin haka Abbansu ya tattarosu suka dawo gida Nigeria.

Rufaida da MK sunyi kuka sun gaji tunba MK ba dan ba karamin sabo yayi da mahaifiyar tasa ba dan har rikesa a asibiti sai da aka yi da kyar aka samu aka shawo kansa ya dawo normal amma ynxu ko maganan ummansa bai so a masa dan duk sai yaji ya tsaneta . Gatansa sune Rufaida da Daddy sai kuma Nani da tun zuwansu Nigeria take taredasu tun MK ba ya sonta hr suka saba inda yanzu yake jinta tamkar mahaifiyarsa, kuma itama tana sonsu tamkar 'yayanta shi yasa Rufaida ke wa Daddynsu sha'awar aurenta.



Zaune suke a dakin Anna, hira suke bnda sabbura da ke gefe tanaiwa kannenta bitar karatu, sallamar wani almajirine ya katsesu yace "wai ana sallama da Sabbura, ko dagowa batayi ba balle ta yi yunkurin tankawa, Shamsiyya ce tace "kace tana zuwa sannan ta dubi inda Sabbura take ta mata ido, sai da ta dan bata lokaci sannan ta tashi ta fice yayinda Shamsiyya ta bi bayanta suna fita Anty Suwaiba ta juyo gun Anna tun kan ta ce wani abu Anna ta daga mata hannu tace " Suby mun gama maganan nan kuma kin nuna mun baza sake dagota ba sabida haka bn son jin komai, cikin sanyin jiki tace "toh Anna bazan sake magana akan wannan batu ba, amma zuciyanta cike yake da haushin kannen nata.

Sabbura na shiga dakinsu shamsiyya ta shigo itama, ita ta tayata shiryawa hrda mata yar kwalliya duk da Sabbura bata so hakan ba, fesheta da turare tayi ta rakota hr bakin kofa sannan ta koma.

Can gefe ta hango shafiq na tsaye jikin motarsa, karasawa tayi cikin takunta a hnkali, shi kuwa tunda ya hangota ya kasa dauke idonsa, komai nata burgesa yake, yanayin tafiyarta ma abun kallone, hr ta karaso bai dauke idonsa a kanta ba, sallama ta mai ya amsa sannan suka dan gaisa tace mai su shiga daga ciki.

Side na Abbanta suka nufa dan dama yace duk sanda ya zo suna zuwa side nasa, kujeru ta aje musu sannan ta tashi ta dauko mai ragowar kunun aya da tayi yana sha suna hiransu, da ya tashi tafia har wajen motarsa ya sa ta rakasa inda ya miko mata wani leda, kin karba tayi, ba ynda beyi da ita ba amma sam taki karba, ya dubeta yace " nasan zakice its too early but ni a wajena hakan ba komai bane, wayace dama na siya miki sabida in nazo ba sai na aiki yaro ba kuma duk sanda wata bukatar yin magana dake ya taso zn kira musamman in nayi kewarki kema kuma zaki iya kirana, duk wata bukata naki da ya tashi zaki iya nemana a waya ni mai yi mikine Abba da kansa ya bn go ahead so bn ga dalilin da zaki ki krban kyautan da ur husby to be ya miki ba, murmushi tayi sannan tace " nagode sosai da wannan kyautar taka amma a gaskia bazan iya karban wannan kyautar taka ba, dalilin kuma bazan iya fadama ba, in gaisawa ce duk sanda naji bukatar hakan zan karbi wayan addana in kiraka da shi amma kayi hakuri dan wannan kyautar ta mun girma.

Ajiyar zuciya yayi yace "toh shikenan, nasan tunda kika ki karba dalilinki zai zamto mai karfi sabida haka bazan tilastaki akan ki karba ba sai dai zan cigaba da aje miki shi har zuwa ranar da zaki bukata. Hango Abbanta da tayi shiyasa ta mai sallama ta shige gida shi kuwa ya tsaya ya jira ya karaso suka gaisa.

Dakin Anna ta wuce ta tarar kannen nata hr sunyi bacci ta dagasu ta gyara musu kwanciyarsu sannan ta hau tattara takaddunsu. Abbane yayi sallama ya shigo dakin duk suka amsa mai, inda Sabbura ke zaune ya nufa ya aje mata wani leda sannan ya juyo yace "Sabbura ga sako ance in kawo miki, yana gama fadin haka ya fice, yana fita Shamsiyya ta zo ta ja ledar dan Sabbura ko kallon ledar batayi ba, ihun da Shamsiyya tayi ya ja hankalin kowa a dakin, rungume Sabbura tayi tana " wow sis am so happy for u, wayace sabo gal kirar Tecno case da aka sawa wayarma kadai abun kallone balle ita wayar kanta, mika mata wayar shamsiyya tayi bata ma yi yunkurin kaima ummarta ba dan tasan mai zai biyo baya, sauran yayyunta kawai  ta nuna wa wayar, anty suwaiba ne ta krbi wayan tana duddubawa tace "Iye irin waya tacema saura kuma ynxu anga ana rike irin wayata a dauka level daya muke, dole ma incanza wayane kawai dan bazai yu ki rike irin wayar dake hannuna ba, warce wayan shamsiyya tayi tace " a tsufar lafiya will hv bn k, bawai a tsaya ayita  maganar da bashi da amfani ba, tashi tayi Anna ta jawota ta zauna tace "Anna da kin bari na jima yarinyarnan ciwo dan sam batada kunya wlh ki ka mun iskanci daddakaki znyi kuma gobe in hanaki binmu abujan, yar gajeriyar dariya shamsiyya tayi tace " in ur dreams kenan, tattara ledan tayi ta ja Sabbura suka br dakin.

A daren ta gama koyawa Sabbura abubuwan kan wayar dan tasan bata iya komai ba, har su watsapp ta bude mata ta koya mata ynda ake chatting sannan shamsiyya ta kwanta ta brta sabida tafiyar da ke gabansu.



Shakuwace sosai ynxu tsakanin Sabbura da Shafiq inda suketa zuba soyayyarsu mai tsafta har manya ma na kokarin shiga ciki Abbansa kawai ake jira ya dawo daga course da yaje a kasar waje a turo. Ba karamin dadi Sabbura taji ba dan ko ba komai zata huta da wahalar gidansu.

~~~~

Rufaida ce zaune a dakinta tana nazarin wani littafi,rufewa naga tayi ta tashi ta fice daga dakin. Hanyar dakin M.K ta nufa dan tun sanda ta kamasa da nicky ba su sake haduwa ba dan kulle kansa yake a daki bai ko fita, a hankali ta tura kofar dakinsa ta gansa zaune ya kurawa wani frame ido bai ma san da shigowarta ba hr ta zo ta zauna ta sa hannu ta krbi frame in taga hoton ummarsu, juyowa yayi yana ganinta yayi yunkurin tashi, kamo hannunsa tayi ta maida shi sannan ta juyo da fuskarsa taga idanunsa sunyi ja ga dukkan alamu kuka yayi, riko hannunsa tayi tace "I knw u miss her, we ol do, cire hannunsa yayi daga nata cikin bacin rai yace " I hate her, n u dnt miss ppl u hate n pls lts not talk abt dis cos u knw how i react abt dat more dan anyone so pls lets not start, jan bakinta tayi tayi shiru har kusan minti uku bawanda ya sake magana sai can ya juyo yace "Yaushe tafiyarki?
" Gobe insha Allah ta bashi amsa, "So u r really going? Kai kawai ta gyada mai, " even after i promised u dt i wil change? Riko hannunsa tayi tace "M.K, i knw u, n lyf da ka dauka its not u n nasan zaka bari, me staying wunt change a thing, kai ba yaro bane u knw wts ryt n wts wrong ba sai an gayama ba if u r rily willing to change u"ll change, n i promise i wil come visit any chance i gt ok", cire hannunsa yayi daga nata bai ko sake kallonta ba ya tashi ya shige toilet, tashi tayi itama ta fita dan tasan ynxu kam ba abunda zata gaya mai yaji.



Cikin shiri Rufaida ta fito da yar trolleynta ta wuce dakin Abbanta, ta jima a ciki sannan suka fito inda shi yayi kasa ita kuwa tayi dakin M.K ta jima tana knocking amma yaki ya bude, wayanta ta ciro ta kirasa tana ji yana ringing amma yaki picking, wucewa kasa tayi kawai inda Abba ke jiranta.

Gefensa taje ta tsaya, dan rungomota yayi ta gefe yans patting nata yace " Yaki saukowa ko, dnt u worry jst gv him time, dagowa tayi tana mai murmushi sannan ta basa hug tace "I will miss u so much Dad n pls batun Nani i hope to hear good news soon, murmushi yayi sannan yace " I will miss u too my princess, n u"ll hear good news cos i will do evrytn dt mks u hapi.

Nani ce ta fito daga side nata ta nufosu, gaisawa sukayi duka sannan ta karbi akwatin Rufaida sukayi waje duka, har wajen driver suka rakota rungume Nani Rufaida tayi tareda cewa ta cigaba da kula da M.K dan ynxu he nids her more dn eva. Sai da sukaga ta fice sannan suka koma cikin gida.

Rufaida na shiga airport ta je ta gama abunda zatayi ta je ta zauna tana jiran a kirasu, bai jima ba kuwa aka kirasu ta tashi ta yi hanyar da zai sadata da inda zata hau jirginsu, juyowa tayi dan taga ko zata hango MK dan duk a tunaninta bazai bari ta tafi basuyi sallama, ganin ba ko alamunsa ya sa ta cigaba da tafia, hr ta sa kai ta sake juyowa ta hango MK ya shigo cikin sauri-sauri gudu-gudu, suna hada ido ya tsaya yana hucin gajia, juyawa tayi taje ta karasa inda yake ta riko hannunsa ta nema musu waje suka zauna, zuwa akayi aka mata magana akan cewa in ta bata lokaci zatayi missing flight nata juyowa Rufaida tayi ta ce ba matsala zata kama next one in.

Kusan minti biyar suka dauka suna zaune sannan MK ya juyo yace "am sorry sis for d way i acted, its very selfish of me a ce in hanaki tafia, i knw in ba dole ba u wunt liv me here am really sorry for trying to stop u frm living, share mai hawayensa tayi tana rarrashinsa har yayi shiru, hira sukayi hr aka sake kiran jirginsu sannan suka rabu yana daga mats hannu hr ya daina ganinta.

Cikin sauri ya bar airport in ya je ya shiga motarsa ya hada kansa da steering ya hau kuka, tunda yake da 'Yarsa bai taba yin nisa da ita ba kuma sun saba sosai shi yasa ynxu duk ya damu, sai da ya sha kukansa sannan ya sa wa motar key ya figeta cikin zafin nama.

Sabbura ta taso daga gidansu Atika kenan tazo daidai gidan nicky ta ga motan MK yazo yayi parking daidai kofar har ya so ya bugeta, tana ganinsa ya fito ya hau buga kofar gidan, batayi mamaki ba dan dama shi bai yi kama da mai hankali ba sai dai batasan rashin hankalin ya kai haka ba, rage tafiyarta tayi dan ganin ikon Allah dan tasan wacece Nicky kusan duk anguwama an santa, gogaggiyar karuwace kuma duk mai shiga gidanta toh ba mutumin arziki bane, gani tayi an bude kofar nicky ta gani daga ita sai wata yar vest sai yar guntun skirt da bai kai gwiwa ba, ganin nicky na kallon gefe ya sa MK juyowa ya ga Sabbura da ta tsaya ta kasa motsi kasa dauke idonsu sukayi duka har sai da nicky ta kama hannunsa ta shigar da shi tareda watsowa Sabbura harara sannan ta rufo kofar.

Sabbura kuwa mamakin knta ta fara ganin ta tsaya kallon abunda bai shafeta ba,gyara daurin nikabinta tayi sannan ta wuce gida.

Share:

RYM 6

🤦🏾‍♀         *Rayuwar*        🤦🏾‍♀

          🙆🏾       *'Ya*    🙆🏾

🙎🏽            *Mace*              🙎🏽

Na B.A. Ladan

♻ *EXCLUSIVE* *WRITERS* *FORUM*

*06*

_Dis page is for ma Admins_
_Maman Ilham_
_Titty luv_
_Hauwa Suleiman (My Kawa)_
_Amiraty( Sista mie)_
_My Luku Luku_&
_My run away Admin Bello Adam Ambursa( please ku tayani cigiyarsa)_
_Kunyi a rayuwa👌🏼, Allah ya barmu tare ya kara dankon zumunci_ *LUSVM*



Xaune take a kofar kitchen nasu tana jira miyanta yayi ta sauke ta raba abinci, Anty Suwaibane ta fito daga dakin Anna cikin daga murya tace "Sabbura baki gama bane? "Saura kadan  Anty, sabbura ta amsa mata " toh kiyi sauri gaskia dan duk yunwa muke ji, Anty suwaiba na gama fadin haka ta koma ciki. 

Cikin nutsuwa ta gama sawa kowa abincinsa a flask ta shigar, a karshe ta dauki na Abbanta tayi sashinsa.

Tun daga bakin kofarsa ta gane yanada baki dan taga takalma. Tsayawa tayi a bakin kofar tayi sallama duk suka amsa mata sannan Abbanta ya mata izini ta shiga, cikin takunta a hankali ta karaso ta aje abincin ta dago dan gaidasu, taga mallam shafiqne da Mal Abakar zuciyanta ba karamin bugawa yayi ba dan duk a tunaninta wani laifin tayi, da kyar ta iya gaishesu ta fice.

Kitchen ta shige ta dauki abincinta ta wuce dakin Anna wajen 'yan'uwanta, tun kan ta karasa take jiyo dariyarsu, da sallamarta ta shiga taga sun juye abincin a kan plate hrda Anna suna ci, gefen kannenta ta zauna inda suma ke cin abincinsu. Har ta gama bata dago ta kallesu ba dan wani zafi da zuciyarta ke mata, hada kayan tayi ta fice dasu sannan ta koma ta dubi kannenta ta ce suje su dau takaddunsu ta musu bitar kratunsu. Da gudu suka fice suna rige-rige, basu jima ba sai gashi sun dawo suka zauna a gabanta ta fara musu karatu suna bi, Anty Saliha ce ta dago tace "a'a baza fa kuma damemu ba, dauki yaran nan kuje can dakin kuyi karatunku, kan ma su tashi Abbanta ya shigo dakin da sallamarsa duk suka juyo tareda amsa mai, kallon Sabbura yayi sannan yace " Kije ana magana dake, kallon juna su anty Suwaiba sukayi suna mamakin wannan abu, Sabbura kuwa bata ma san sunayi ba ta tashi ta wuce dakinsu ta sanya hijabinta ta fito, Abbanta ta gani tsaye a kofarta ya dubeta cikin kulawa yace "kije suna falona, cikin jin kunya ta bi ta gefensa ta wuce.

Cikin tsiririyar muryanta ta musu sallama tareda shiga falon Abbannata, dan nisa da su ta zauna tareda sake gaidasu daga can bata sake cewa komai ba, Mal Abakar ya dubeta yace "Sabbura ga abokina na kawo miki kuma kan muzo sai da muka tunkari Abba kuma ya bamu goyon ba,dafatan kema zaki krbemu hannu bibbiyu dan mu da zafinmu muka zo dafatan zaki krbemu, murmushi tayi tareda sadda kanta kasa tana watsa da yatsunta sannan a hankali tace " Tunda kunyiwa Abba magana kuma ya amince nima na amince, Allah ya tabbatar mana da alkhairi, "amin suka amsa mata sannan Mallam Abakar ya fita ya basu wuri, hira kadan sukayi sannan suka fito ta rakosa inda Mallam Abakar ke jiransa ta musu saida safe ta koma ciki.

Dakin Anna ta nufa dan duba ko su samira basuyi bacci ba ta karasa musu karatun, hr ta sa hannu zata daga labulen taji Anty Suwaiba na cewa " Anna wa kuma 'yar taki ta samu bamu da labari haka, Allahsa dai baso take ta riga yayyunta aure ba dan mai dunia zatace gamu gardan-gardan a gida ba ko mashinshini a ce ta rigamu
aure.

Shamsiyya ce ta tari numfashinta tace "toh sai me in ta rigamu auren, ai hakan ba haramun bane kuma aure shi nufine na Allah in Allah yace zakayi ko mijin kawarki sai kiga kin aura *(kawa da ke nake🤣)* kuma anan ba yanda Abba baiyi a cire miji ba ku ka ki sabida haka bnga dalili da za ake wannan maganan ba, Anty Suwaiba ta mata wani irin kallo sannan tace " wannan da kike karetan nan ko dai kema auren zakiyi, "in ma zanyi laifine, ko so kike in cigaba da zama har sai kunyi aure, kunda ba niyya yi kuke da ba, dama banso fada yanzu ba amma tunda magana ta taso toh bara inyi kowa yaji, kan mu koma skul iyayen Haidar zasu zo gaisuwa immediately after na gama kuma muyi auren mu, baki bude su Anty Suwaiba ke kallonta sannan ta juyo gun Anna tace " Anna kina jin meh yarinyar nan ke fada, baku san bakin jini zaku shafa mana ba ko, toh wlhy tun wuri ku kau da wannan tunanin dan bazata sabu ba, bakusan illar kanwa ta riga yaya aure bako, bakusan hakan zai iya sawa mu kare rayuwarmu a cikin gidan nan bako, wani yar dariya Shamsiyya tayi tace "Anty Suwaiba wannan duk camfine in kinyi imani da Allah kuma ke mai yarda da kaddarace toh faruwan hakan bazai baki tsoro ba kuma duk abunda zaku ce bazai hanani aurena ba kuma da tuntuni najima da yin auren nan amma na tsaya jiranku amma ynxu kam bnga dalilin da zai sa har sai na jira kunyi aure tukun nayi ba, ganin fadane yake shirin barkewa yasa Anna cewa " Suby rabu da ita, meh abun fada in sun rigaki auren, kr ki manta fadin da ake cewa God saves d best for d last, wani jinkirin alherine sabida haka ki kwantar da hnkalinki besides bn gaji da kallonku ba n ko ba komai zan huta da bakin cikin wannan kanwar taku dan duk sanda na ganta nakanji raina ya baci duniyan duk ta mun baki abun farin cikine a wajena in aka ce zata tafi ta br gidan nan so bn son ki kara tada hnkalinki a kan wannan batu, zama tayi a gefen Anna tareda rungumarta shamsiyya kuwa ta juya ta bar dakin, Sabbura na jin motsin wani na shirin fita ta bar wajen da gudu tayi bayan gidansu inda taje ta takure tana kukarta a hankali, dolene ta nisanta kanta da 'yan uwanta da mahaifiyarta dan wannan tsana da suke mata ya wuce misali, ko bata son Shafiq ta yadda ta aureshi ko dan ta bar gidansu hakan ne kawai zata samu kwanciyar hankali koh ta huta da azabar gidansu, ji tayi an tsunkuya a kanta ta dago ta ga Abbantane sake fashewa tayi da kuka tana "Abba dan Allah kaji tausayina ka kaini gun mahaifiyata dan ban yadda Anna ce ta haifeni ba, Abba ka mun rai ka sadani da mahaifiyata ko sau dayane inji dumin jikinta, inji ya soyayyar uwa yake, kalamanta saida ya sa Abba hawaye ya dubeta yace taso kizo Sabbura

Falonsa suka zauna, sai da yaga ta bar kuka yace " Sabbura banga laifinki dan kin fadi hakan ba amma ki yarda dani in na ce miki Annace mahaifiyarki, bakida wata uwa sai ita Sabbura, "Toh Abba mesa ta tsaneni? ta tambayesa cikin kuka, ajiyar zucia yayi yace " Sabbura bazan iya fada miki dalilin da ya sa mahaifiyarki ta tsaneki ba dan jin hakan zai iya sa kema ki tsaneta ki tsani wanda yayi sanadiyar sa ummarki ta tsaneki, in Allah ya nufa watarana zan fada miki amma a yanxu ba abunda zance dake sai dai ince ki cigaba da hakuri nasan da zafi amma wataran insha Allah zaki ci moriyar hakurin nan taki kuma bnso ki sake dago wannan zancen kinji uwata, kai ta kada sannan yace share hawayenki kije ki kwanta, har ta sa kai zata fice ya sake kiranta ta juyo yace "batun malaminku nayi bincike kuma naga yarone nitsatstse kuma dan gidan mutuncine sabida haka na basa goyon baya amma sauran zabi na gareki amma ina miki kwadayin aurensa dan nasan zai kulamun da ke, murmushi tayi cikin jin kunya tace "Abba nagode sosai, nasan bazaka taba son abunda zai cutardani ba, duk abunda ka aminta da shi nima na aminta da shi, zabinka shine zabina, murmushi yayi dan yaji dadin furucinta yace " Allah miki Albarka Sabbura tashi kije.

Kanta na kasa ta zo ta wuce bata ma lura da Baba Saude da ke zaune ba sai da ta yi tsawa tace "Ke!! zo nan, Sabbura ta juyo cikin tsoro a take jikinta ya hau rawa, durkushewa tayi tana yarfa hannu ganin itacen da ke hannun Baba Saude ta dubeta tace " wato kinyi girman da har zaki na kawo kawaye cikin gidan nan da har zasu ci min mutunci koh,

hada hannayenta tayi waje biyu ta hau bata hakuri tace "Baba Saude kiyi mun rai wlhy wlhy ba sata nayi ba kuma ma tace zata zo ta baki hakuri, dariyar mugunta Baba Saude tayi tace " ba abunda zai hanani jibgarki, wato dama ke a tunaninki wasar tsere da kike mun mantawa nayi da ke, duk taraki nake amma yau watar cin ubanki ya kama,daga itacen tayi zata maka mata ta ji an rike tareda janyewa daga hannunta ta juyo taga Shamsiyya rike da icen tace "ana auran ubanta kuma ake zagin uban nata, ai toh da sai kije kiyi da shi ba ki tsaya kinayi da yar cikinki ba, ynxu ke Baba Saude ko kunya bakiji ki sa yarinya a gaba kiyita jibga, rashin imaninki ma ya wuce misali kuma wlhy bar ganin kina matar ubana ba a taba nawa inyi shiru sai mu kwashi 'yan kallo nida ke a gidan nan, in kuma kince mu gwada toh bismillah, sanin halin shamsiyya sarai zata aikata yasa Baba saude shiga daki tana " ba laifinku bane laifin ubanku ne da ke daure muku gindi.

Karasawa tayi inda Sabbura ke durkushe tana kuka ta dagota sukayi daki.

Har suka shiga dakin Sabbura bata bar kuka ba, da kyar ta rarrasheta tayi shiru, ta dubeta tace "Sabbura ynxu dama zaman da kike a cikin gidan nan knan, bazaki tashi ki tsayawa kanki ba sai ki aje jiki tayi ta jibgarki toh wlhy gwara ki daina dan wannan sakarcine, share kwalla tayi tace " Adda Shamsiyya bazaki taba ganewa ba kawai dai a bar maganan, kuma maganar da kika mata ba wai ta hakura bane, kuna tafiya nasan sai ta huce a kaina shi yasa nake rokonki da duk abunda zata mun dan Allah kr ki mayar mata da magana ko ba komai matsayin uwa take a wajenmu musayar yawu da ita rainini bazan so kuma a dalilina kike hakan ba har azo ana fushi dake sabida haka pls ina rokonki ki bari, tana gama fadin haka ta dauki sallaya da hijabinta ta fice dan bata so maganar yayi nisa.




♨♨♨♨♨♨♨♨

Cikin shiri Rufaida ta sauko sai kamshi take, falon Abbansu ta shige inda ta tarar da shi yana karanta jarida ta zo ta zauna gefensa tareda gaishesa, ya dubeta cikin zolaya yace "amarya a gidan shureim irin wannan kyau haka, daria tayi tace " Daddy bnda zolaya dai, yace "ai ma princess ko ynxu aka je gasar miss world ba ko shakka ke zaki ci dan duk dunia dia isn't any one as beutiful as u bt dts besides ur mum ya fada cikin alamun da ya nuna ya ji zafin maganar, saukar da knta kasa tayi dan tasan duk lokacin da aka ambaceta duk suna shiga wani yanayi, dagowa tayi tace " Abba dama wata magana naxo muyi, gyara zamansa yayi yace "ina jinki princess, " dama a kan Nani ne, sai kuma tayi shiru, Daddy yace go on princess, a hankali tace "Abba me zai hana ka auri Nani, zamanku haka a gidan nan bn jin dadi n shs bn wt us tun da muka dawo Nigeria kuma duk kowa ya yaba da halinta, shs gonna b a perfect wife to u n a mum to us kuma na san in na tafi zata tayani kulawa daku, ajiyan zucia Daddy yayi sannan yace " Nagode princess da kulawarki garemu nida lil bro inki, bawai banki shawararki ba but i will think about it kafun ki tafi zaki ji amsa na, dan hugging nasa tayi tace " i hope to hear a positive answer bari in shiga hau in duba dan rikicin tun jiya ya kulle kansa a daki, dariya daddy yayi yace "kunfi kusa shi yasa bn shiga ba kr anjima inji kunya, dariya itama tayi sannan ta haura sama.

Ganin baya daki ya sa ta sauko ta shige dakin Nani ta tarar tana sallah zama tayi ta idar ta juyo tace " Nani shigowa nayi in tambayi dan wajen naki dan tun jiya yake fushi dani, murmushi tayi sannan tace "Rufaida ashe dama ke ki tabo mun shi, toh maza kije kiyi biko, yana can dakin da ke gaban gida dan in abu ya damesa can yake zuwa yayi zamansa, tashi Rufaida tayi tace " Nanj barinje toh, wannan dan naki sai ku gwara ma inyi in tafi in barku ku karata sannan ta fice.

Kai tsaye ta shiga dakin bako sallama, mutuwar tsaye tayi a bisa abunda ta gani cikin daga murya tace MK what the f...................!


♻ *Billy Ladan* ♻

Share:

Sunday 6 August 2017

Rayuwar Ya Mace

🤦🏾‍♀         *Rayuwar*        🤦🏾‍♀

          🙆🏾       *'Ya*    🙆🏾

🙎🏽            *Mace*              🙎🏽

Na B.A.Ladan

♻ *EXCLUSIVE* *WRITERS* *FORUM*

*01*

Zaune take akan sallaya tana lazimi tana jira a kira assalatu dan ta tashi ta gabatar da sallar asuba, tana zaunen har aka kira sai da taji masallatai sun fara sallah sannnan itama ta tashi ta gabatar da sallanta. Jingina kanta tayi da bango dan ta dan huta kafun ta kama aiki, kaman daga sama taji aka fara kiranta "Sabbura! " Sabbura!!
A hankali ta tashi ta nade sallayan ta dubi Anna da ke zaune tana nazirin wani takadda ta ce "Anna ina kwana? Wanda ta kira da Anna ko dagowa batayi ba sai ma dai ta cigaba da abunda take, fita tayi dan inda sabo ta saba da wannan hali na mahaifiyar tata.

Tana fita ta ci karo da Baba saude fuskan nan murtuk ba ko alamun daria, a hankali sabbura ta karasa ta dan russuna tace " Baba Saude ina kwana? Bugu ta kai mata tana "Munafuka in ban kwana ba kya ganni a nan, shegiyar ya da naketa ihu dama kina ina?, sunkui da kai tayi tana rikeda kanta inda Baba saude ta buge, a hankali tace "Baba Saude Sallah fa nake, " Toh sallau kullum aka taboki sallah sai kace kinfi kowa ibada anjima kuma kice zaki dauki tsirarun kafarki kice zaki makaranta toh wallahi idan kinga kin fita a gidannan kin gama ayyukanki ne gaba daya, ban damu ko zaki latti ba sabida haka yi maza ki kama aiki, Komawa daki Baba Saude tayi yayinda Sabbura ta wuce ta hura wuta, shayi ta fara daurawa sannan ta debo tulin dankalin hausawa ta fara ferewa.

Abbanta ne ya shigo dawowarsa daga masallaci knan ya ganta tana aiki kai kawai ya kada sannan ya karaso inda take, tana jin kafar mutum ta juyo tana ganin Abbantane ta dan sauko daga kan kujerar da take tace "Abba ina kwana?  " lafia lau sabbura ya amsa mata sannan yace "har kin hau aiki, toh ina sauran yan uwan naki? " basu tashi ba Abba ta basa amsa, "maza je ki tada su dan wannan aikin ya miki yawa, " Abba ba sai an tadasu bama ai ba yawa ynxu zn gama.

"Ki dai tadasu Sabbura cewar abbanta, " a'a Abba wlhy abarsu zan gama ai na saba, "toh shikenan Sabbura dan ya san abunda take gudu yace " Allah ya miki albarka Sabbura, ki cigaba da hakuri wataran zaki ci moriyarsa, "Amin baba nagode ta amsa mai  ya tashi ya shige zuciyansa cike da tausayin yar tasa.

Tea na tafasa ta dauki flask ta sa wa kowa nasa sannan ta soma soya dankalin bai dau lokaci ba tagama tayi sauce sannan ta daura ruwan wanka dan lokacin sanyine sannan ta fara share cikin gidan tas ta hado wanke wanke tayi, kafun ta gama har ruwan yayi ta sauke sannan ta shige dakin Anna cikin sauri ta gyara ta sa turare ta fice dan tada kannenta, sai da ta musu wanka sannan itama ta yi ta shiryasu gaba daya ta samu musu breakfast nasu a cooler dan sun so suyi latti, dakin Anna suka shige kannanta Shahid da Sameera suka gaida Anna ta amsa musu cikin sakin fuska sannan ta ja purse nata ta ciro hundred naira guda biyu ta basu, Samira sarkin baki tace " Anna na Anty Sabbura fa? Ko kulata Anna bata yi ba ganin zata dameta yasa ta daka mata tsawa tace " zaki fara shegen nacin maganartaki ko, in baki bace mun a nan ba kema sai in karbe kudin nawa, yi tayi kaman zatayi kuka tazo ta fada jikin yayar tata, Sabbura ta dagota tana rarrashinta ta kamo hannun Shafiq suka fice.

Tana sa kafarta cikin tsakar gidan ta hango Baba Saude zaune bakin kofarta tana ganinta tace "Wannan 'ya da bakin hali kike, ynxu abincin ma sai mun biyo mun dauka toh maza sake hannun yarannan ki kai musu abinci kuma ki jirasu su gama kan ku wuce, in ba bakin hali da mugunta irin taki ba meh ya hanaki kai musu abincin, ba tareda ta sake hannun kannen nata ba tace "Baba Saude wlhy mantawa nayi kuma ai inba yau ba bn taba fashin shigarwa ciki ba, tunda yau basu gani ba ai kamata yayi su fito su dauka, Salati Baba saude tayi tana tafa hannu tace " Oh ni Saude, Sabbura har kinyi girman da ina fada kina fada toh wlhy maza kizo ki kai musu abincin nan kuma kafarki kafarsu in yaso duk kuyi lettin a taru a daka ai dama can muguntarki yasa kikayi hakan dan a jibga mun 'ya'ya ko? Toh wlhy sai dai a hada dake, "Yi hakuri Baba saude cewar Sabbura, wlhy ba da gangan nayi ba amma gaskia sai dai su fito su dauki abincinsu kuma ni baxan iya jiransu ba dan sai na biya na ajesu sameera zan wuce, Tashi Baba Saude tayi tayo kan Sabbura ta fara ja da baya dan ta san meh hakan ke nufi, jiyo Muryan Abbanta tayi yace "ke Sabbura ba makaranta zakuje ba zo maza ku wuce, Godia tayi wa Allah a ranta da ya kawo abbanta sannan ta bi gefen Baba Saude da take hararanta tana mata kallon zaki dawo ki sameni ne ta fice, har ta kai kofa Abbanta ya kirata ta ja ta tsaya tareda juyowa, karasowa yayi ya bude zip na jakarta ya sa mata abu a ciki sannan ya rufe ya musu addu'a sannan suka fice. Tabe baki Baba Saude tayi ta shige daki

Napep ta tara musu suka shiga sai da ta aje su itama ta yi hanyar ajinsu, dakali ta nema ta zauna dan ta kagu ta ga meh Abbanta ya sa mata a jakar, tana budewa taga yar tsohuwar dari biyu take taji hawaye ya fara zuba mata ta kankame jikinta ta zauna tana ta sharban kuka yayinda take jin son mahaifinta nata sosai tareda jin tausayin kanta, dama bata san ya zatayi ba dan dama ko kudin ruwa bata da shi ga dankali da shegen kwaran mutum dole sai da ruwa. A duk lokacin da tuno da rashin sa'arta a rayuwa ta kanji dunia ya mata baki, kukan ne kawai ke sa ta danji sauki shi yasa ta zauna take kukarta.
Ace wanda ta tsuguna ta haifeka take nuna ma tsananin kiyayya da tsana mai yafi wannan rashin sa'a a dunia, tana cikin kuka taji ance "Dan Allah ina tambaya mana, dagowa tayi ta watso mai idanunta masu fisgar hankali da sukayi ja sabida kuka, suna hada ido ta kawar da kanta, ynda ya ganta ya sashi yace " sorry i cn jst ask sum1, share hawayen nata tayi tace "no ina jinka, saurayin yace " dama office na principal naku nake nema, come with me tace dashi yana kan hanyata ta zuwa aji zan iya nuna ma, suka jera suna tafia kowa da abunda ke yawo zuciyarsa har suka iso office in ta dubesa tace "gashinan, batareda ta jira ya ma mata godia ba ta bar wajen dan zuwa aji, bayanta ya bi da kallo yana tunanin ko meke damunta haka kawai yaji yana son sanin danuwarta dan ya share mata hawayenta gashi ko tsayawa batayi ba balle ya tambayi sunanta, yana tsaye a wajen hr ta bace mai, ji yayi an dafasa ance " Shafiq har ka iso, juyowa yayi yace "eh uncle ynxu zuwana, mu shiga daga ciki toh cewar uncle in nasa sannan ya bude musu office in suka shige.






*02*

*Sabbura* *Idris* *Liman* shine asalin sunarta
Ya ta hudu a wajen Alhaji Idris Liman.
Su shida Anna ta haifa, Saliha, Suwaiba, Shamsiyya, Sabbura, Shahid sai Autarsu Samira yayinda Kishiyar Anna Saude keda yara hudu
Rahama, Rayyan, Rabi'u sai Nawar.

Iyayensu haifaffun yan Maidugurine anan jihar Borno kuma suma duk anan aka haifesu.

Alhaji Idris karamin dan kasuwane inda yake da shagonsa a nan monday market duk da ba wani karfi yakeda ba yana iya kokarinsa wajen ya kyautatawa iyalansa kuma ya sa yaransa a makaranta amma duk wannan bai hana Baba Saude surutu a koda yaushe ba dan ita haka Allah yayita bata da godiyar Allah, gata mafadaciya da wuya a wayi gari bata samun abun fada dadin dadawa kuma ita kullum a gida take sabanin Anna da ke koyarwa a wata secondary school dan dama ita da iliminta ya aurota kuma da ba dun kaddara ba da ba abunda zai sa ya auro Baba Saude dan Anna mace ce mai hankali, wanda ta san ya kamata matsalar shi daya da ita wannan *Karan* *Tsana* da ta daura wa yar ta Sabburah



♨♨♨♨♨♨♨♨

Kamar Kullum ta tashi ta gama ayyukanta dan yau tana da islamiya. Bakwai daidai  ta gama ta fito cikin shiri, doguwar hijabi ce purple har kasa sai safar hannu da na kafa da ta sa sai kuma nikabinta da ta riko a hannu, tana daura niqabin Baba Saude ta dago labulen dakinta tana mata wani kallo ita kuwa Sabburah bata ma lura da ita ba, tana juyowa ta ganta tsaye ta dan russuna tace "Baba Saude ina kwana? rike gaisuwar ki bata wannan nake ba cewar Baba Saude, da kike shirin fitan wa zaiyi karin kumallo? " Ai na gama komai Baba Saude Sabbura ta bata amsa ta kara dacewa "Har miyan rana nayi in na dawo kawai shinkafa zan daura, hakan ba karamin kular da Baba Saude yayi ba dan ita burinta a kullum tana musguna mata, nan ta fara tunanin aikin da zata sata kawai dan ta sa tayi latti dan tasan hukuncin hakan dukane, har Sabbura tayi gaba ta fara tafia Baba Saude ta ce " Toh sarauniyar sauri ai ban gama ba, ina yau mukayi dake zaki wanke mun ban daki da safe, ajiyar zucia Sabbura tayi dan ta san nufin Baba Saude kan ma ta tanka Abbanta ya sako kai tana ganinsa ta saki murmushi a zuciyanta tace "Here cums ma  saviour, kallonta yayi yace Wuce ki tafi bata ko kalli gefen Baba Saude ba ta fice cikin sauri. Baba Saude ta hau surfa bala'i " Ai dama Malam kai kake sa yaran nan su rainani in bahaka ba taya za'ace zan sa Sabbura aiki ka wani ce ta fice ta tafi ai duk wannan ni kake janyowa raini, kada kai yayi sannan yace "Saude taya yarinya ta shirya zata makaranta ki tsuro mata da aiki, aikin ma da kikasan bata karewa da wuri bace kina tausayawa yarinyan nan wlhy ina guje miki ranar da hakkinta zai biki, kyautatawar da take miki 'yayanki ma basu miki amma sam baki sassauta mata kullum burinki ki musguna mata, taresa tayi tace " Kaga Mallam ya isa, dama ba isa a tabo yar gaban goshinka ba sai ka kama wa mutum wa'azi ai tunda ka hanata yi mun aikin shikenan ai, ynxu fisabilillahi ina zan je in bukatata ya tashi , Yace "Ai ga Rahama ita meh zai hana ta wanke miki ban dakin, wani kallo ta mai sannan tace " Alhaji kai ma dai fada kake,Rahaman nawa take, zan dai jira Sabburan, kada kansa yayi yace " ai ice tun yana karami ake tankwarasa, duk abunda Sabbura zatayi Rahama zatayi tunda shekara ta bata, da a ce kina koya mata ai da tuni ta iya,tunda kin zabi jiran nata ai sai ki jira,yana kaiwa nan ya juya ya shige dakinsa yayinda Baba Saude ta bisa da harara tana "Munafakin maza kawai, ai da yar gaban goshinne da yayanta ko muryarka ba za a ji ba, inga mai hanani sa wannan shashashar aiki.




Sabbura kuwa tana fita ta wuce gidan kawarta Atika, a falo ta samesu itada ummarta suna karyawa a plate daya, zama tayi tareda gaida ummar Atika ta zauna tana jiranta ta gama su tafi, kura musu ido tayi tana sha'awar yanda suke cin abinci tare har da yar hiransu da dariya, hawaye ta ji ya taru a idanunta dan tasan wannan wani abu ne da bazata taba samu ba dan ko wuri daya basu zama da mahaifiyarta balle har hira ya shiga, kauda kanta tayi ta dan share kwallar da ya zubo mata.

Ba karamin bata musu lokaci Atika tayi ba dan sa hijabi kadai ma ta bata lokaci, suna isa kuwa sukaga an fara taran letti, Sabbura ta zaro ido dan ko kadan bata son abunda zai taba wannar farir fatarta tata mai shegen laushi dan abu kadan sai kaga jikinta ya pashe dan ko wanki mai yawa in tayi zakaga hannunta ya tsatsage.

Cikin tsoro suka karasa Atika ta mika hannunta aka bata bulala biyar Sabbura da ke gefe kuwa sai tsalle take tun kan ma a zo kanta, taki sam ta mika hannunta har Atika ta gaji ta shige ta barta, malaminsu kuwa yace ba yanda za a yi ta shiga bai daketa ba, hakan yasa ta ja gefe ta zauna tana kuka tana rokonsa.

Wata motace ta zo tayi parking a gefenta, tana ji aka fito tareda rufe motar ya zo dab inda take zaune taji ance "Malam ya ita wannan bata shiga ba take zaune a kai, " wlhy Malam Shafiq letti tayi kuma taki miko hannu a daketa shine nace ta zauna ta tayani hira dan bazan daki saura in barta ba cewar malaminsu, wanda aka kira da Shafiq yace " Hakane Mallam kayi gaskia sannan ya dubi inda Sabbura take yace "malama kalli nan, ya sunanki? Ta dago tareda cewa " Sabbura, tayi saurin ganesa as saurayin da suka hadu a school yayinda shi kuwa yake tunanin ina ya taba jin muryannan dan niqab da ke fuskarta ya hanashi ganin komai nata ji tayi yace "taso ki biyoni, cikin rawar jiki ta tashi ta bi bayansa suna shiga ya dubeta yace " ki wuce aji amma nan gaba ki kula, godia ta mai sannan ta wuce aji,

Tana shiga ta hango Atika sai dariya take mata maimakon ta je wajenta sai ta nemi wani waje ta zauna, Atiqa na ganin haka ta taso tazo ta zauna gefenta tace "Haba kawata ta kaina fushi ake danine, harara Sabbura ta mata tace Atika in na sake biya miki ki canzan suna ai da ba dan keba da bnyi latti ba amma daga yau ta kare kowa yake zuwa shi daya, nan Atika ta hau bata hakuri amma ko ta kulata dan ta gama kular da ita, matsowa Atika tayi ta fada mata abu a hankali naga ta yi daria tareda dan tureta tace " Ni barni Atiqa ban son ji muraja'a zanyi, sake matsowa tayi ta mata magana a kunne wanda ya kawo barkewan hira tsakaninsu har basu san lokacin da malami ya shiga har yayi rubutu kan allo ba, Sabbura sai zuba take, jin ajin yayi tsit ya sa su juyowa sukaga duk su ake kallo hr Malamin cikin sauri ta sauke niqabinta dan shigowarta aji ta daga yayinda ta tashi tana bawa malamin hakuri, shi kuwa zuciyansa fal murna dan ya hadu da wanda ta hana zuciyarsa sukuni, cikin sakin fuska yace "ki zauna in an tashi ki sameni a office in malamai, amma inaso ku kula aji musamman ta islamia ba wajen hira bane idan malami bai shigo aji ba sai kuyi muraja'a bawai a kafa majalisar hira ba ko a tsaya chatting da ture turen abu a waya sabida haka ku kula. Ni sunana Shafiq Kuma naxo ne a madadin malaminku na kira'a, yace in baku hakuri tafiyar gaggawace ta samesa shine ya turoni gashi kuma naga lokaci ya dan kure sabida haka karatu kawai zan kara in yaso in ya dawo duk ku hada haddan ku basa, nan suka bubbude Qur'aninsu ya kara musu karatu cikin muryarsa mai dadin sauraro, kafin ya fita sai da ya sake tunawa Sabbura batun ta zo ta samesa sannan ya fice.




Karfe shabiyu suka tashi Sabbura taja hannun Atika tace muje kawa, Atiqa tace "kiran mallam fa? Sabbura tace " sai dai gobe in na gansa inje amma yau kam sai dai ya hakura dan nasan minti daya na kara anan ina kara wa kaina bala'i ne dan yanzu nasan abunda ke jirana a gida kenan sabida haka muje kawai gwamma hukuncin da zai yanke mun akan bala'in Baba Saude, tabe baki Atika tayi tace "Lalle Sabbura kina hakuri, yaushe zan tsaya matar uba ta mai dani baiwa a gidan ubana, murmushin takaici Sabbura tayi sannan tace " Atika bazaki ganeba iyayena ma basu tsira ba sai ni, dole yasa kika ga nake abunda nakeyi dan gudun magana wa mahaifina, uwata da ta haifeni da ya kamata ita zata na tsayawa  ta karemun hakkina bata damu dani ba toh wat choice do i have, kuma Atika a dane abunda Baba saude ke mun ke damuna amma yanxu na saba ke dai kawai ki dai tayani addu'a, da haka sukayi sallama kowa ya shige gida zuciyan Sabbura cike fal da fargaban abunda zata tarar.

Share:

Blog Archive

Search This Blog

Featured post

RYM 12

         Rayuwar                     'Ya            Mace            Na Billy Ladan *EXCLUSIVE* *WRITERS* *FORUM* *12* bintladan.bl...

Contact Form

Name

Email *

Message *